Close Menu
ABKNEWS 24
  • Home
  • Business
  • Entertainment
  • Features
  • News
  • Politics
  • Security
  • Sports
  • More
    • Agriculture
    • Climate
    • Tech
    • Write Up
    • Video
  • HAUSA
    • Ilimi
    • Kasuwanci
    • Labarai
    • Lafiya
    • Nishadi
    • Siyasa
    • Tsaro
    • Wasanni
Facebook X (Twitter) WhatsApp Telegram
Facebook X (Twitter) Instagram
ABKNEWS 24ABKNEWS 24
Subscribe
  • Home
  • Business

    KNSG Collaborates with Zirconex for Establishment of Standard Mining Laboratory

    August 28, 2025

    SOLLONG – A NEW PHONE YOU WILL BUY WILL GET YOUR MONEY BACK AND CONTINUE TO EARN MONEY IN IT FOR A YEAR

    August 26, 2025

    SOLLONG – SABUWAR WAYAR HANNU DA ZAKA SAYA TA MAYAR MAKA DA KUDIN KA KUMA KA CIGABA DA SAMUN KUDI A CIKINTA HAR TSAWON SHEKARA DAYA

    August 26, 2025

    USSD Deductions Under Fire: Why Failed Transactions Still Attract ₦6.98 Charges

    August 21, 2025

    QNET Warns Fraudsters, Backs Ogun Gov’t Over Crackdown

    October 12, 2024
  • Entertainment

    From novels to blockbusters: Nollywood’s next frontier

    October 14, 2024

    Prioritise having kids over marriage for career success – Laide Bakare advices ladies

    October 10, 2024

    Qausain TV appoints Adam A. Zango as Director-General

    October 8, 2024

    Patrick Doyle Criticises Davido’s Attire During Visit To Olu Of Warri

    October 7, 2024

    British fencer Akinyosoye switches allegiance to Nigeria

    October 7, 2024
  • Features

    Mai Martaba Sarkin Daura Alhaji Dr. Umar Farouk Umar ya nada Sheikh Abdulkadir Jiyali a Matsayin Sarkin Takutahar Kasar Hausa.

    July 23, 2026

    KEYAMO, MUSAWA CONFIRMED AS SPEAKERS AT 9TH NATIONAL TOURISM TRANSPORTATION SUMMIT & EXPO 2026: By Ado Salisu 

    July 23, 2026

    NSSF President Joseph elected ISF Africa continental president.

    July 23, 2026

    Defamation Against DSP Barau, Institutional: By Abba Anwar

    July 23, 2026

    CHANGE OF NAME: I formally known and called as ABDUL SHEHU YUSUF, now wish to be called and addressed as ABDUL SHEHU YUSIF. Former documents remain valid. General public to take note.

    July 23, 2026
  • News

    KEYAMO, MUSAWA CONFIRMED AS SPEAKERS AT 9TH NATIONAL TOURISM TRANSPORTATION SUMMIT & EXPO 2026: By Ado Salisu 

    July 23, 2026

    CHANGE OF NAME: I formally known and called as ABDUL SHEHU YUSUF, now wish to be called and addressed as ABDUL SHEHU YUSIF. Former documents remain valid. General public to take note.

    July 23, 2026

    Showcase What You Will Do Not Baseless Opposition…Tinubu Projects In The North Are Traceable, Kwankwaso.

    July 22, 2026

    Allegations of Political Interference Trail Investigation into Death of Kano Man.

    July 21, 2026

    Controversy Deepens as Senator Barau Mounts Intense Pressure on Police Following the Death of an Alleged Notorious Killer.

    July 21, 2026
  • Politics

    2027: Jamilu’s Victory, the pathway to progress of Gombe citizens

    July 15, 2026

    ADC Shahuci Ward Reaffirms Expulsion of Hajiya Naja’atu Muhammad, Rejects Claims on Kano Party Structure.

    July 12, 2026

    Tinubu’s Picking Of Shettima: Final Onslaught On The North..The Region Has Been Gotten, Musa Illiyasu Kwankwaso.

    July 11, 2026

    Niger Delta group backs President Tinubu for 2027.

    July 9, 2026

    Da Dumi Dumi: Babbar Kotun Tarayya Ta Tabbatar da Jagorancin Mark a ADC, Ta Kuma ci Tarar Abejide.

    July 2, 2026
  • Security

    THE SAFE RESCUE OF THE ABDUCTED SCHOOL CHILDREN AND THEIR TEACHERS IN OYO STATE IS A VICTORY FOR NIGERIA. WE MUST NEVER SURRENDER OUR NATION TO TERROR – DAYO ISRAEL .

    July 11, 2026

    Police not responsible for delay in establishment of state police — IGP.

    June 24, 2026

    Military rescues ex-defence spokesperson Rabe’s wife from bandits.

    June 15, 2026

    NSCDC Kano Command Dismisses Five (5) Volunteer Personnel for Unethical Conduct and Indiscipline.

    June 2, 2026

    CP Balarabe Sule rtd, expressed his happiness over the way stakeholders in Kano have come together to bring about lasting peace in the State.

    May 17, 2026
  • Sports

    NSSF President Joseph elected ISF Africa continental president.

    July 23, 2026

    Aghazu confident as Team Nigeria heads to Glasgow with medal-hungry athletics squad.

    July 23, 2026

    Oyo FA, Pillar of Sports in Partnership to Organize a Capacity Building Seminar for Football Coaches

    July 23, 2026

    Inter- Union Soccer Tourney: Pro-Chancellor tasks Northwest University athletes on NUGA Games: By Ado Salisu 

    July 21, 2026

    Team Nigeria Embarks on Final Journey from Aberdeen to Glasgow for 2026 Commonwealth Games: By Ado Salisu

    July 20, 2026
  • More
    1. Agriculture
    2. Climate
    3. Tech
    4. Write Up
    5. Video
    6. View All

    HJRBDA, Bichi and 3rd Anniversary of Tinubu’s Renewed Hope Agenda on Food Security.

    June 12, 2026

    Kano Govt Intervenes After ‘The Historica Nigeria’ Exposes Alleged Tree Felling at ARTV.

    June 7, 2026

    Agriculture: Nigeria, Vietnam Sign Strategic Pact to Boost Cashew Trade, Technology Exchange

    November 8, 2025

    Gwamnati ta fara shirin tabbatar da ƙananan manoma sun amfana da sabbin taraktocin Belarus.

    October 29, 2025

    NiMet Predicts Three-day Thunderstorm, Downpour Nationwide

    October 14, 2024

    The Sad Story Of Flooding In Niger State

    October 9, 2024

    Flood: Yobe Govt approves over N1.4bn for 25, 500 victims

    October 8, 2024

    Climate Change: Fishers Raise Alarm Over Insecurity On Seafood

    October 3, 2024

    SOLLONG – GET A SOLLONG BLOCKCHAIN DEVICE PHONE TODAY AND EARN IN USDT FOR ONE YEAR.

    August 28, 2025

    Partnership with JICA has put Nigeria’s startup ecosystem in global map -DG NITDA

    October 14, 2024

    EVENTS FOR THE WEEK 14TH TO 20TH OCTOBER, 2024. – Centre for Information Technology and Development

    October 14, 2024

    INVITATION TO APPLY: Sustainable Enterprise Challenge Project in Kano State Phase 2 – Centre for Information Technology and Development

    October 12, 2024

    Defamation Against DSP Barau, Institutional: By Abba Anwar

    July 23, 2026

    From Enlightenment to Eclipse: Nigeria’s Democracy in an Age of Shadows: By Abbati Bako,psc,bsis,UK Alumnus

    July 19, 2026

    REBUILDING PUBLIC TRUST IN LEADERSHIP: THE NASIR IDRIS EXAMPLE IN KEBBI STATE: By Ibrahim A Jombali

    July 17, 2026

    Abdulaziz, the Arewa Media Summit, and Tinubu’s Renewed Hope Agenda – By Shehu Mustapha Chaji.

    July 12, 2026

    THE DANGER OF LEADLESS SOCIETIES AND THE NEED FOR RESPONSIBLE DEMOCRACY.

    May 16, 2026

    Mai Martaba Sarkin Daura Alhaji Dr. Umar Farouk Umar ya nada Sheikh Abdulkadir Jiyali a Matsayin Sarkin Takutahar Kasar Hausa.

    July 23, 2026

    KEYAMO, MUSAWA CONFIRMED AS SPEAKERS AT 9TH NATIONAL TOURISM TRANSPORTATION SUMMIT & EXPO 2026: By Ado Salisu 

    July 23, 2026

    NSSF President Joseph elected ISF Africa continental president.

    July 23, 2026

    Defamation Against DSP Barau, Institutional: By Abba Anwar

    July 23, 2026
  • HAUSA
    1. Ilimi
    2. Kasuwanci
    3. Labarai
    4. Lafiya
    5. Nishadi
    6. Siyasa
    7. Tsaro
    8. Wasanni
    9. View All

    Zaku iya tsayuwar Arfat a gidajen ku kamar yadda yazo a Hadisin Manzon Allah S.A.W – Imam Khalifa Sheikh Yusuf Ahmad Gabari

    May 24, 2026

    Alhassan Ado Doguwa ya bayyana ilimi a matsayin Kashi bayan cigaban Kowace Al’umma

    May 12, 2026

    Kwadaye da fushi nadaga cikin abubuwan dasuke jefa mutane cikin halaka. Farfesa Aminu Isma’il Sagagi.

    February 14, 2026

    Hukumar shirya jarrabawar shiga manyan makarantu tace laifi ne dalibi ya boye matakin karatun da yake.

    February 8, 2026

    Mummunar Gobarar Kasuwar Singa: Anyi Asarar Biliyoyin Kudi Yayin da Gobarar ta Kone Shaguna sama da 1,000 ana gab da Shiga watan Ramadan.

    February 15, 2026

    Ramadan 2026: Farashin Zobo, Tsamiya, da Kayan Kamshi Ya Yi Tashi a Kasuwannin Kano.

    February 11, 2026

    Gobara ta tashi tareda Kone wasu Shaguna a Kasuwar Singa dake Kano a Najeriya

    November 10, 2025

    ’Yan Bindiga Sun Sace Mata 5 Ciki Har Da Masu Shayarwa A Kano Najeriya .

    November 10, 2025

    Mai Martaba Sarkin Daura Alhaji Dr. Umar Farouk Umar ya nada Sheikh Abdulkadir Jiyali a Matsayin Sarkin Takutahar Kasar Hausa.

    July 23, 2026

    Rt. Hon. Alhassan Ado Doguwa ya kudurin gaggawa ga Majalisar Wakilai ta Kasa domin ta Sahale a sake Gina Gadojin Yankin Yaryasa dake Karamar Hukumar Tudun Wada: Auwalu Ali Sufi

    July 10, 2026

    Jam’iyyar ADC a Kano tayi Watsi Da Kwamitin Riko na Naja’atu Muhammed, Ta Kuma Bayyana shi a Matsayin Haramtacce ne.

    July 7, 2026

    ADC ta rusa shugabancin jam’iyyar na Kano tare da kafa kwamitin riƙo.

    July 6, 2026

    Ana neman al’umar Annabi SAW su taimaka domin ceto rayuwar Hajiya Khadija da Sayen Magani. Domin karin bayani 08065164420 – 08031824749

    June 30, 2026

    Shugaba Tinubu ya sake bada Umarnin a Kara Mutum 20,000 Domin Daukar su aikin “Yan Sanda Kari akan 30,000 – Hon. Aliyu Wakilai Boya

    December 3, 2025

    Gwamnatin Tarayya zata karbi Asibitin Kansa da Gwamnatin Ganduje ta gina domin Mayar dashi karkashin kulawar AKTH – Hon. Kabiru Abubakar (Abba Bichi)

    November 23, 2025

    Gwamnatin Kano Ta Tabbatar Da Ɓullar Cutar Shan Inna

    October 30, 2025

    Shin Yaya kuke Kallon Sabon Shirin Film din “KADDARA” ko zai iya disashe farin jinin Shirin “LABARINA”???

    December 11, 2025

    Dawowar Jarumar Kanywood Nafisa Abdullahi Nigeria domin fara daukar Shirin “KADDARA”

    December 11, 2025

    Za’a Daura Auren Jaafar Muhammad Kabiru da Ruqayya Abubakar sai Kuma Nafisa Muhammad Kabiru da Zubairu Umar Ibrahim (Malan)

    October 27, 2025

    MAULUD: SHAHARARREN MAWAKIN NAN JAMILU JADDA GARKO YA SAKI SABUWAR WAKARSA MAI TAKEN “ANNABIN RAHAMA” A YAU JUMA’A

    September 12, 2025

    Halacci Gadon Bacci: Daga Hajiya Fatima Abdullahi Dala, APC Women leader Kano.

    July 10, 2026

    Jam’iyyar mu ba wata ƙungiya ce ta mutum daya ba – NDC.

    June 8, 2026

    “Kai ma ka taba zama yaro na a siyasa” — Ganduje ya mayar wa Kwankwaso martani

    May 29, 2026

    Matashin Dan Siyasa Hon. Musa Sani Indabo ya Mika Form din Takararsa na neman zama Dan Majalisar Tarayya mai wakiltar Wudil/Garko a NDC.

    May 19, 2026

    Wasu ‘Yan Bindiga Sun Yi Fashin Ragunan Layya A Kano.

    May 21, 2026

    DSS ta kama wata mata a Kano da ke safarar alburusai ga ƴan ta’adda a Katsina.

    April 2, 2026

    Rundunar yan sanda tace ta dakile harin lakurawa a jihar kebbi

    February 8, 2026

    Gwamnatin jihar Kogi ta rufe kasuwanni da tashoshin mota saboda matsalar tsaro.

    February 8, 2026

    Jami’ar bayero ta lashe gasar kwallon kwando ta jami’o’in yankin Arewa maso Yamma 

    February 8, 2026

    Ahmad Musa ya yi ritaya daga Super Eagles bayan shekaru 15 yana buga kwallo.

    December 17, 2025

    Ahmad Musa ya yi ritaya daga Super Eagles bayan shekaru 15 yana buga kwallo.

    December 17, 2025

    Yaya kuke ganin karawar da Super Eagle ta Nigeria zasuyi da Kasar Congo a yau lahadi domin samun damar shiga gasar cin kofin Duniya???

    November 16, 2025

    Mai Martaba Sarkin Daura Alhaji Dr. Umar Farouk Umar ya nada Sheikh Abdulkadir Jiyali a Matsayin Sarkin Takutahar Kasar Hausa.

    July 23, 2026

    Rt. Hon. Alhassan Ado Doguwa ya kudurin gaggawa ga Majalisar Wakilai ta Kasa domin ta Sahale a sake Gina Gadojin Yankin Yaryasa dake Karamar Hukumar Tudun Wada: Auwalu Ali Sufi

    July 10, 2026

    Halacci Gadon Bacci: Daga Hajiya Fatima Abdullahi Dala, APC Women leader Kano.

    July 10, 2026

    Jam’iyyar ADC a Kano tayi Watsi Da Kwamitin Riko na Naja’atu Muhammed, Ta Kuma Bayyana shi a Matsayin Haramtacce ne.

    July 7, 2026
ABKNEWS 24
Home » Yadda HE Garo Ya Wakilci Gwamna Fiye Da Wadansu Mataimakan Da Gwamnoninsu Cikin Kwanaki 47.

Yadda HE Garo Ya Wakilci Gwamna Fiye Da Wadansu Mataimakan Da Gwamnoninsu Cikin Kwanaki 47.

By ABK NEWSJune 21, 2026 Write Up 10 Mins Read
Share
Facebook Twitter Email Telegram WhatsApp

GridArt 20260621 221727918

Yadda HE Garo Ya Wakilci Gwamna Fiye Da Wadansu Mataimakan Da Gwamnoninsu Cikin Kwanaki 47

– Yabo ga Gwamna wajen karfafa yarda da amana da zartaccen dogaro

Daga Abba Anwar

Kamar dai yadda kowa ya sani ne, Majalisar Dokokin Jihar Kano ta tantance kuma ta tabbatar da Maigirma Murtala Sule Garo, a ranar 27 ga watan Afrilu, 2026. Bayan da tsohon Mataimakin Gwamna Maigirma Aminu Abdussalam Gwarzo ya ajiye aiki dan kashin kansa.

Bayan nan kuma sai a ka rantsar da Garo ranar 5 ga watan Mayu, 2026. Daga lokacin zuwa yau 20 ga watan Mayu, ya cika kwanaki 47 cif a kan karagar mulki kenan.

Daga lokacin da a ka rantsar da shi zuwa yanzu ya wakilci Gwamna Maigirma Abba Kabir Yusuf a wurare da yawan gaske. Ban sa wurare irin na gaisuwar mara lafiya da gaishe-gaishen mutuwa da daure-dauren aure ba. Saboda tun ma kafin lokacin ya zama Mataimakin Gwamna dama yin hakan dabi’arsa ce.

Kafin in nutsa cikin ire-iren wuraren da ya wakilci Gwamna din, zan fara da cewar, dama tun daga ranar rantsuwarsa, bayanin da ya yi a wajen ya nuna sakankancewar sa ga sabon tsarin nan na “Kano First Agenda.” Kan abubuwan da su ka shafi kyautata harkokin lafiya da ilimi da noma da samar da aikin yi ga al’umma.

Tun daga jawabin sa na karbar wannan mukami, ya nuna a fayyace cewar, shi fa mabiyi ne mai biyayya da karbar umarni ba wata tangarda. To tun daga nan fa ya aza harshashin kyakkyawar alaka tsakanin sa da Maigirma Gwamna.

Wani babban abin lura kuma shine daidai lokacin da wasu da yawa daga cikin Mataimakan Gwamnoni na wasu jihohin su ka wakilci Gwamnoninsu sau uku ko sau biyu ko sau daya ko ba ko daya ma, a cikin wadannan kwanaki 47, shi kuma a daidai lokacin ya wakilci Gwamna Yusuf sau wajen 10.

Hakan da nake fada, ba kuma wai ina tuhumar ragowar Mataimakan Gwamnonin ba ne. A’a sai dai kawai ina kwatanta yawan wakilcinsu ne da na Maigirma Garo a wadannan kwanaki 47. Ba dadi ba ragi. Illa iyaka.

Ranar 8 ga watan Yuni, ya wakilci Gwamna lokacin da Jakadun Kungiyar Gamayyar Turai, wato “European Union (EU) Ambassadors” su ka kai ziyarar ban girma gidan gwamnatin jihar Kano. Washegari kuma 8 ga watan Yuni din, ya kara wakiltar Gwamna wajen taron Gwamnonin Arewa Maso Yamma tare da wadannan Jakadu, kan abubuwan da suka shafi tsaro da zaman lafiya da cigaban kasa.

Ranar 13 ga watan Yuni ya wakilci Gwamna a rufe wata gasar kwallon kafa da a ka yi a filin wasa na Sani Abacha dake Kofar Mata. Karkashin shirin “North-West Veterans All-Star Renewed Hope.”

A wani bikin yaye dalibai a makarantar sojojin ruwa dake karamar hukumar Dawakin Tofa, wato “Navy Logistics College,” wanda a ka yi ranar 18 ga watan Yuni, Maigirma Mataimakin Gwamna ya wakilci Gwamna a wajen. A matsayin babban bako. Jawabin da ya yi a wajen kuma ya kara tsima dakarun sojojin kan aikinsu da kishin kasa.

A wani kirari da na yi masa a halin da a ke ciki shine, “Garo Ka Iya Mataimakin Gwamna,” ya kara wakiltar Gwamna a ranar 27 ga watan Mayu, lokacin da ya kaddamar da wani shirin NNPC da ya shafi harkar iskar Gas na kamfanin Kanawa Gas Ltd.

Wani babban abin lura kuma shine, lokacin da wasu Mataimakan Gwamnonin shiyyoyi shida na kasar nan ke da tarihin wakiltar Gwamnonin su sau uku uku ko biyu ko dai-dai, wasu ma ba wannan maganar, a cikin kwanaki 47, amman shi Maigirma Garo ya wakilci Gwamna har sau kusan 10.

A daidai hakan ne kuma ya wakilci Gwamna a wani taron Gwamnonin Arewa Maso Yamma kan tsaro, wanda kungiyar Gwamnonin shiyyar su ka shirya. An yi taron ne ranar 29 ga watan Mayu, a jihar Kaduna.

A asibitin Hasiya Bayero kuma lokacin da a ka kaddamar da shirin samarwa asibitin gadon marasa lafiya guda Dari Biyar (500), bangaren yara da mata, ya wakilci Gwamna a wajen. An yi bikin ne ranar 3 ga watan Yuni.

Sannan kuma ya wakilci Gwamna wajen yin wani gagarumin taro da kungiyoyi masu zaman kansu kan harkar kasafin kudi da inganta aiki da shi. Wanda a ka yi ranar 7 ga watan Yuni din dai.

Ranar Dimukuradiyya kuma, wato 12 ga watan Yuni, ya kara wakiltar Gwamna a wajen bikin da a ka yi a filin wasa na Sani Abacha dake Kano. Lokacin da har addu’o’i an yi wa kasa.

Maigirma Garo ya je wajen duba aikin titin Kwanar Dangora-Zaria da na Dala-Kofar Mata, a madadin Gwamna, wanda a ka yi ranar 15 ga watan Yuni. Yayin da ya karawa masu yin aikin kaimi wajen ganin sun hanzarta kammala aikin.

Sai kuma ranar 18 ga watan Yuni din dai ya je wani taro da masarauta a Gidan Rumfa kan shirye-shiryen bukukuwan Sallah cikin tsaro da kwanciyar hankali. A wajen taron ma ya wakilci Maigirma Gwamna ne.

Saboda kuma na kara jan hankalin masu karatu su san cewa akwai aminci da yarda tsakanin Gwamnan Kano da Mataimakin sa, sai na yi bincike kan yadda wasu Mataimakan Gwamnanonin shiyyoyi 6 na kasar ne suke kan abinda ya shafi wakiltar Gwamnoninmu. A cikin wadannan kwanaki 47.

Amman fa yin hakan ba ya nufin ina kallon su da wani abu ba. Kawai dai so nake na danganta yadda kyawun alaka da sakankancewa da juna dake tsakanin Gwamnan Kano da Mataimakin sa. Tun daga lokacin da a ka rantsar da shi abin ya fara daga kyakkyawan tushe.

Bari na fara da Arewa Maso Yamma tukuna. Dama na fara da maganar Maigirma Garo. Saboda haka bari na fara da Mataimakiyar Gwamnan Jihar Kaduna, wato Maigirma Hadiza Sabuwa Balarabe.

Maigirma Balarabe ta wakilci Gwamna Uba Sani sau uku a wadannan kwanakin da nake magana. A ranar 18 ga watan Mayu, ta wakilci Gwamna a wani gagarumin taron da ya shafi cigaban jihohin Arewa Maso Yamma. Haka nan kuma a dai cikin watan na Mayu ne ta kara wakiltar Gwamnan a wajen kaddamar da tashin maniyyata aikin Hajji a sansanin Alhazai na Mando. Na ukun kuma shine da ta wakilce shi a filin wasa na Kafanchan wajen kaddamar da takarar Sanata Sunday Marshall Katung.

A sashen Arewa Maso Gabas kuma, misali a jihar Bauchi, Mataimakin Gwamna Maigirma Auwal Jatau, ya wakilci Gwamnan sa sau uku a wadannan kwanaki da nake magana a kai. Ranar 3 ga watan Yuni ta wakilci Gwamna a taron Hukumar Raya Arewa Maso Gabas, wato “North East Development Commission.” Da kuma babbar makarantar nan ta kauyen Dungal. Sannan ranar 1 ga watan Mayu ya wakilci Gwamna wajen kaddamar da shugabannin jam’iyyar PDP na Arewa Maso Gabas.

A jihar Adamawa kuma Mataimakin Gwamna Farfesa Kaletapwa George Farauta ya wakilci Gwamna wajen shirin tallafawa jama’a na “PAWECA Fintiri Business Wallet Phase 4 Disbursement,” a garin Yola.

Ya kara wakiltar sa a wajen bikin nadin sarauta na mutanen Batta, a fadar Hama Bata, a garin Demsa. Sau kuma lokacin nada sababbin manyan sakatarorin ma’aikatun gwamnati da kuma nada wani Kantoma, a Yola.

Sannan a Arewa Ta Tsakiya kuma na dauki jihohin Nassarawa da Benue. Mataimakin Gwamnan Nassarawa Dr Emmanuel Agbadu Akabe ya wakilci Gwamna lokacin kaddamar da wani shiri na bayar da tallafin kudi ga mata, wato “Rural Women Special Cash Grant.” Da a ka yi a dakin taro na Akwe Doma, a garin lafiya. Sannan kuma ya wakilci Gwamna zuwa babban ofishin jam’iyyar APC na kasa.

A jihar Benue kuma Mataimakin Gwamna Dr Samuel Ode, mni, ya je bikin harkokin noma, wato “Agricultural Mechanisation Outgrower Programme,” da a ka yi a babban birnin jihar, Makurdi. Sai kuma wata walima da a ka a kwalejin sojoji “Armed Forces Command & Staff College,” a Makurdi din dai. Ya kuma wakilci Gwamna wajen hira da yan jarida kan taron sasantawa na jam’iyyar APC a jihar. Bayan nan sai wakilci wajen bikin binne Mama Elizabeth Apochi, a garin Owukpa, cikin karamar hukumar Ogbadibo.

A shiyyar Kudu Maso Yamma Mataimakin Gwamnan Osun Maigirma Kola Adewusi ya wakilci Gwamnansa ranar 18 ga watan Yuni a wani taron DAWN, da a ka shirya ma shugabannin ma’aikatan gwamnatocin Kudu Maso Yamma. Sai kuma a lokacin da kungiyar Gwamnonin shiyyar ta shirya taron Mataimakan Gwamnonin shiyyar kan hadin kan yankin.

Ranar 5 ga watan Yuni Mataimakin Gwamnan dai ya wakilci Gwamnan a wani taron lafiya na “Osun Art Surge HIV Project” a garin Osogbo. Da wani taron ma na lafiya na “US CDC/PEPFAR-funded HIV/AIDS project.” Lokacin da kwamitin neman zaben Gwamna Adeleke ya kai ziyarar ban girma ga fadar Ooni na Ife a Ile-Ife, Mataimakan Gwamna ne ya wakilci Gwamna a wajen.

A jihar Lagos kuma Mataimakin Gwamna Maigirma Obafemi Hamzat sau daya ya wakilci Gwamna a cikin wadannan kwanakin da muke magana a kai. Shine lokacin da a ka yi bikin ranar ma’aikata, wato 1 ga watan Mayu, a filin wasa na Onikan. Amman bincike ya nuna cewar shi Hamzat ya na ta abubuwan da su ka shafi takarar sa ta gwamna ne a shekarar 2027 mai zuwa.

A shiyyar Kudu Maso Gabas kuma a jihar Enugu, Mataimakin Gwamna Maigirma Ifeanyi Ossai, ranar 10 ga watan Yuni ya wakilci Gwamnansa a wajen kaddamar da neman takarar Sanata mai wakiltar Enugu North, a zaben cike gurbi, da a ka yi a karamar hukumar Igbo-Etiti

Sannan a jihar Abia kuma Mataimakin Gwamna Maigirma Ikechukwu Emetu, a ranar 1 ga watan Mayu ya wakilci Gwamna a wajen taron duban gyaran tsarin mulki na kasa daga mahangar Kudu Maso Gabas.

Daga bangaren Kudu Maso Kudu kuma Mataimakin Gwamnan jihar Cross River Peter Odey a ranar 14 ga watan Mayu ya wakilci Gwamna a taron Majalisar Zartaswa ta Jiha, da a ka yi a ofishin Gwamna.

A jihar Rivers kuma Mataimakin Gwamna Maigirma Ngozi Odu ta wakilci Gwamna a ranar ma’aikata, wato 1 ga watan Mayu. Da a yi a Isaac Boro Park, na Port Harcourt.

Maganar dai gaba daya a nan ita ce, lokacin da wasu daga cikin Mataimaka Gwamnoni ba sa samun dama daga wajen Gwamnonin su na wakilcin su. Duk lokacin da su Gwamnonin ba sa gari. Sai kuma wata rana su tura Shugabannin Majalisun jihohin nasu su wakilce su. Yayin da watakila da gangan za ka ga sun tura Mataimakan nasu wani abu a wajen jihohin. Amman fa a jihar Kano abin ba haka yake ba. Ya sha banban da abinda a ke gani a wasu jihohi. Wannan abin a yabawa Maigirma Gwamna Yusuf ne.

Kuma duk wanda ya yi nazarin yadda Gwamna Yusuf yake tura Mataimakinsa Garo wakilci a wurare da dama haka a cikin wadannan kwanaki 47, hakan na nuni da cewa tabbas Juma’ar da za ta yi kyau daga Laraba a ke gane ta. Ba abinda ya rage mana a matsayin mabiya sai addu’ar Allah Ya ci gaba da hada kansu, wajen kawo ayyukan ci gaban wannan jiha ta mu mai albarka. A gaba dayan zango mulkinsu.

Anwar ya rubuto wannan daga Kano
Lahadi, 21 ga watan Mayu, 2026

Share. Facebook Twitter LinkedIn Email Telegram WhatsApp

Related Posts

Defamation Against DSP Barau, Institutional: By Abba Anwar

From Enlightenment to Eclipse: Nigeria’s Democracy in an Age of Shadows: By Abbati Bako,psc,bsis,UK Alumnus

REBUILDING PUBLIC TRUST IN LEADERSHIP: THE NASIR IDRIS EXAMPLE IN KEBBI STATE: By Ibrahim A Jombali

Abdulaziz, the Arewa Media Summit, and Tinubu’s Renewed Hope Agenda – By Shehu Mustapha Chaji.

Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne: ‎ ‎Daga Abba Anwar ‎

SECURING OUR FUTURE: A CALL TO SUPPORT THE NORTHERN NIGERIA SECURITY TRUST FUND (NNSTF).

Add A Comment
Leave A Reply Cancel Reply

Latest Posts

Mai Martaba Sarkin Daura Alhaji Dr. Umar Farouk Umar ya nada Sheikh Abdulkadir Jiyali a Matsayin Sarkin Takutahar Kasar Hausa.

July 23, 2026

KEYAMO, MUSAWA CONFIRMED AS SPEAKERS AT 9TH NATIONAL TOURISM TRANSPORTATION SUMMIT & EXPO 2026: By Ado Salisu 

July 23, 2026

NSSF President Joseph elected ISF Africa continental president.

July 23, 2026
Advertisement
© 2026 ABKNEWS 24. Developed by: ENGRMKS & CO.
  • Home
  • Get In ToAhmad Musa ya yi ritaya daga Super Eagles bayan shekaru 15 yana buga kwallo.uch
  • Privacy Policy

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.