
Majalisar Malamai (Shura) ta Kano ta gayyaci malamin addinin Islama bisa zargin yin Kalaman Batanci ga Annabi Muhammad (SAW).
Majalisar Shura ta Kano ta gayyaci fitaccen malamin addinin Musuluncin nan Sheikh Lawan Abubakr (wanda aka fi sani da Malam Lawan Triumph) domin ya amsa koke da ake zarginsa akai da yin kalaman batanci ga Annabi Muhammad (SAW).
Majalisar, wata kungiya ce mai ba da shawara kan shari’ar Musulunci da Gwamnatin Jihar Kano ta kafa, ta kuma gayyaci masu shigar da kara da su gabatar da shaidun da ke tabbatar da zargin nasu.
Da yake jawabi bayan kammala zaman majalisar, sakatarenta kuma kwamishinan kasuwanci, zuba jari da kasuwanci, Shehu Wada Sagagi, ya tabbatar da cewa an samu koke da kararraki guda takwas daga kungiyoyin Musulunci da na farar hula daban-daban da suke zargin malamin da Kalaman wulakanta Annabi Muhammad SAW.
A cewar Wada Sagagi, wasu daga cikin zarge-zargen sun hada da ikirarin cewa Sheikh Lawan Triumph ya Fadi wasu kalamai da basu dace ya furtasu ba ga Fiyayyen Halitta.
Kungiyoyin da suka hada da Safiyatul Islam ta Najeriya da Kungiyar Samarin Tijjaniyya da Interfaith Parties for Peace and Development da Sairul Qalbi Foundation, Habbullah Mateen Foundation, limaman Masallatan Juma’a da Kwamitin Malaman Sunnah (Kano), da Multaqa Ahbab Alsufiyya ne suka shigar da karar.
“Mun sake duba koke-koke kuma mun yanke shawarar gayyato wadanda suka shigar da karar da kuma Sheikh Lawan Abubakar, wadanda suka shigar da karar za su fara yin karin haske kan ikirarin nasu, daga nan kuma za a ba wa malamin dama ya amsa,” in ji Sagagi.
“Majalisar za ta tantance lamarin sosai bisa tsarin shari’ar Musulunci, sannan ta shawarci gwamnatin jihar da hakan.”
Ya kuma bukaci dukkan bangarorin da su kaucewa ayyukan da za su iya tada zaune tsaye ko kuma kawo barazana ga zaman lafiyar al’umma, yana mai jaddada cewa majalisar za ta yi aiki a cikin huruminta tare da mai da hankali kan yin sulhu.
Batun zagi har yanzu wani lamari ne mai matukar muhimmanci a arewacin Najeriya. A karkashin dokar manyan laifuka ta tarayya, laifi ne da za a iya yanke hukuncin daurin shekaru biyu a gidan yari.
Sai dai a jihohin da ke aiwatar da dokar laifuka ta Shari’a, ciki har da Kano, zagi na iya daukar hukuncin kisa.
A shekarar 2020, wata kotun shari’ar Musulunci a Kano ta yanke wa mawaki Sharif Yahaya Aminu hukuncin kisa ta hanyar rataya bisa zarginsa da aikata sabo.
Hakazalika, a shekarar 2022, wata kotun shari’a ta koli ta yanke wa wani malamin addinin Islama Abduljabbar Kabara hukuncin kisa bisa irin wannan tuhuma.

