Tinubu bai cire tallafin man fetur ba da tuni Nijeriya ta tsiyace — SUNUSI LAMIDO SUNUSI
Muhammadu Sanusi II, ya bayyana cewa da gwamnatin tarayya ba ta cire tallafin man fetur ba, da tuni ƙasar ta tsiyace.
Ya ƙara da cewa tallafin man fetur dama ba abu ne da zai dawwama ba, kuma da shugaba Bola Tinubu bai cire shi ba da tuni ƙasar ta tsiyace .
Jaridar DAILY TRUST ta rawaito cewa Sarkin ya bayyana haka ne a bikin masu waƙoƙin zube, mai suna Kano International Poetry Festival (KAPFEST) karo na biyu da aka gudanar a Kano a jiya Asabar

