Screenshot 20251003 204854 Lite

Matthew Kukah, babban limamin Katolika na Diocese na Sokoto, ya ce Najeriya ba za ta iya kawo ƙarshen ta’addanci ta hanyar amfani da sojoji kaɗai ba.

Kukah ya bayyana haka ne a ranar Alhamis yayin da yake nazari kan littafin “Scars: Nigeria’s Journey and the Boko Haram Conundrum” da tsohon shugaban hafsoshin tsaro, Lucky Irabor, ya rubuta.

Ya ce dogaro da dabarun soja na yaƙi da ta’addanci ba su samar da zaman lafiya mai ɗorewa ba, saboda Boko Haram akida ce, ba wai barazanar makamai kaɗai ba.

“Na tsawon shekaru, muna da Operation Lafiya Dole, Operation Restore Order, Operation Hadin Kai, Operation Safe Haven, da sauran su,” in ji shi.

“Amma duk lokacin da ɗaya ta kasa, sai a ƙaddamar da wata sabuwa. Wadannan hare-haren soja ba su kawo ƙarshen Boko Haram ba saboda ba za ka iya yaƙi da ra’ayi da bindiga kaɗai ba.”

Kukah ya ce bayyana Boko Haram cikin ma’anar soja kaɗai yana rufe hanyoyin samun bayanai da kuma mafita marasa tasirin soja da suke da muhimmanci wajen gina zaman lafiya.

Ya bayyana cewa Boko Haram na ɗaukar yaƙinsu a matsayin jihadi, kuma da yawa daga cikin mayaƙansu suna ganin mutuwa shahada ce, abin da ke sa ba su damu da gargadin soja na da aka saba ba.

Kukah ya yi nuni da babi na 11, 12 da 13 na littafin Irabor, waɗanda suka jaddada muhimmancin sasanci, shugabanci nagari, adalci da warkar da ƙasa a matsayin sharuɗɗan samun tsaro.

Share.
Leave A Reply Cancel Reply

Exit mobile version