Screenshot 20251001 102037 Samsung Internet

Bayo Onanuga, mai ba wa Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu shawara na musamman kan yaɗa labarai, ya yi kakkausar suka ga Kabiru Tanimu Turaki, shugaban wani bangare na jam’iyyar PDP.

 

A ranar Talata, Turaki ya nemi Shugaban Amurka, Donald Trump, da ya tsoma baki a rikicin da ke ci gaba tsakanin bangarorin jam’iyyar PDP.

 

Onanuga ya bayyana wannan kira a matsayin abin ƙyama da kuma babban laifi na cin amanar ƙasa, yana mai cewa wannan abin da Turaki ya aikata “ba zai taɓa gogewa ba a tarihin siyasar Najeriya.”

 

Ya ce “Ba za mu taɓa mantawa da wannan bidiyon ba, ranar da wani ɗan siyasa a Najeriya ya nemi a yi wa ƙasarmu katsalandan daga ƙasar waje, duk saboda rikicin cikin jam’iyyarsu.”

Share.
Leave A Reply Cancel Reply

Exit mobile version