IMG 20250904 WA0015

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya bar Abuja a yau, Alhamis 4 ga Satumba, domin fara hutun shekara ta 2025.

Sanarwar da fadar shugaban ƙasa ta fitar ta bayyana cewa shugaban zai yi hutu na kwanaki goma a Turai, inda zai shafe lokacin sa a tsakanin ƙasashen Faransa da Birtaniya kafin dawo wa Najeriya.

Mai Bawa Shugaban Ƙasa Shawara na Musamman kan Harkokin Bayani da Tsare-tsare, Bayo Onanuga, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a yau.

Domin neman Karin bayani ko saka muku talla sai a tura mana Sakon Whatsapp ta wannan lambar 08027324462 ko a abknaisa100@yahoo.com

Share.
Leave A Reply Cancel Reply

Exit mobile version